Posts

Rayuwata

Image
Alhamdulillah! "Wa'amma Bi-ni'imati Rabbika Fahaddis" Ina godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki a bisa tarin ni'imomi da yayi min masu tarin yawa acikin rayuwata, waɗanda ba zan iya lissafa su ba, saboda yawan su ya wuce duk yanda nake tunani, wanda babu abun da zan ce da Ubangijina sai dai na kasance mai godiya a gare shi akodayaushe, tare da bin dokokin sa, da kuma bin umarnin sa acikin dukkanin al'amuran rayuwa ta.. Kaɗan daga cikin tarin ni'imomin da Allah Maɗaukakin Sarki Ya yi min a rayuwa ta, waɗanda nake matuƙar alfahari da su akodayaushe su ne kamar haka; -Ni'ima ta farko da Allah Maɗaukakin Sarki Ya yi min ita ce, da ya halicce ni a cikin tsatson Musulunci gaba da baya, wanda nake bin tafarkin addinin Musulunci, tare da bin sunnar fiyayyen halitta Manzon tsira, Annabin rahama, Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam, wanda ba ni na tsarowa kaina kasancewa akan wannan tafarki ba, Ubangiji ne Ya ni'imta hakan a tare da ni. -Ni'ima ta biyu...

Komai ya yi farko zai yi ƙarshe

Image
Rayuwa kenan. A lokacin da na kammala karatu ba ma kowa nake ɗaukar wayar sa ba, saboda a lokacin ina matuƙar ji da kaina, ni kawai a tunani na ai na zama wani fitacce. Ko da chatting muke yi da mutum, to fa zai ga ƙaryar turanci, a dole wai ni ga ɗan boko, bayan kuma ɗan turancin na wa ma bai fi cikin cokali ba. To amma fa daga lokacin da duniya ta sako ni a gaba, 1k ta ringa burgeni tare da bani sha'awa, saboda ba ni da wanda ina zaune zai bani ita, to a sannan ne fa na ƙara fahimtar dalilin da yasa taken Nijeriya ya ƙare da "So help me God" saboda a lokacin ban da taimakon Allah Ta'ala babu abun da nake nema. A wancan lokacin duk wani portal na bayar da tallafi ko na aiki da aka buɗe, to fa sai da na cike shi. Na halarci screening da interview ya yi sau Goma ba tare da na samu ba, amma duk da haka ban sare ba, na ci gaba da cikewa duk bana samu.  Da ƙyar na samu Npower a shekarar 2016, inda aka tura ni wani Primary Health Care da ke wani ƙauye, wanda ni...

Who is Adamu Kazaure?

Image
Adamu Sani Kazaure, popularly known as Adamu Kazaure or Ɗan Almajiri, was born on 23rd October 1994 in the Kazaure Local Government Area of Jigawa State. As a young, he is willing to contribute his quota to changing the society, he always shared his ideas with the society and most importantly stands against injustice, and adheres to humanitarian activities. He served a lot in areas that gave him joy and happiness. He served humanity in various forms, he made a lot of friends and helped in various forms, worked on transforming his community and the progress is being made every single day. He also focused on less privilege. He wants to be able to convince other youths that they are the leaders of tomorrow, and they can all change the society by uniting as one and contributing valuable ideas by amplifying their voices to make the world a better place for them. He attended some courses and conferences, even though he is a science student, and started his career at Islamic School (Makaranta...